1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Angela Merkel za ta sake yin takara a zaben 2017

November 20, 2016

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta bayyana wa manyan jiga-jigai na jam'iyyarta ta CDU cewar za ta sake tsayawa takarar neman shugabancin gwamnatin Jamus a shekara mai zuwa a karo na hudu.

https://p.dw.com/p/2SyNK
Angela Merkel kandidiert erneut
Hoto: Getty Images/S. Gallup

Wannan dai sanarwa  ta kawo karshen rade-radi na cewar ko Merkel da ke zama mace mai karfin fada a ji a duniya za ta sake tsayawa takarar.Duk da sukar da wasu masu zabe a kasar ta Jamus suka yi kan tsarin shugabar gwamnatin  na 'yan gudun hijira, ana kallon shugabar gwamnatin a matsayin wata jigo a cikin EU.Kungiyar ta EU ta girgiza dai bayan ficewar Birtaniya daga cikinta yayin da a bangaren guda aka zabi Donald Trump a matsayin shugaban Amirka mai jiran gado.Shugabar gwamnati Angela Merklel dai ta bayyana haka ne bayan tattaunawa da mambobin jam'iyyarta ta CDU a birnin Berlin. Abin da ke share fage na taron jam'iyyar a watan Disamba da ke tafe.