1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An ɗage taron ƙungiyar ƙasashen Larabawa

August 12, 2012

Ministocin harkokin waje na ƙungiyar haɗa kan ƙasashen Larabawa sun so tattauna batun naɗa wanda zai gaji Kofi Annan a matsayin mai shiga tsakani a rikicin Siriya.

https://p.dw.com/p/15oOR
Arab League members, with from left to right at front, Turkey's Foreign Minister Ahmet Davutoglu, Morocco's Foreign Minister Taib Fassi Fihri, Qatari Foreign Minister Hamad bin Jassim and Egyptian's Nabil Al Arabi President of Arab League, as they attend the Arab League foreign ministers meeting in Rabat, Morocco, Wednesday, Nov. 16, 2011. Foreign ministers from the 22-member Arab League nations on Wednesday are expected to formalize their weekend decision to suspend Syria for refusing to end its bloody crackdown against anti-government protesters. (Foto:Abdeljalil Bounhar/AP/dapd)
Hoto: Reuters

Sanarwa wacce matamaikin magatakardan ƙungiyar, Ahmed Ben Helli ya baiyana, na cewar an dage taron wanda aka so gudanarwa a birnin Djeeddah na Saudiyya,ya zuwa wani lokacin da ba saka rana ba, saboda tiyata da aka yi wa yerima Saoud Al Faycal a ciki, ministan harkokin waje na Saudiyya dake fama da rashin lafiya.

Taron dai, ya so tattauna batun zaɓar mutumin da zai maye gurbin Kofi Annan a matsayin manzan ƙasashen na larabawa da Majalisar Ɗinkin Duniya a Siriya ,wanda wa'adin aikin sa ke kammala a ƙarshen wannan wata.Kuma ana kyautata zaton cewar tsohon ministan harkokin waje na Aljeriya Lakhdar Brahimi shi ne zai gaji Kofi Annan ɗin.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita       : Mohammad Nasiru Awal