1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi tir da kalaman shugaban Iran Ahmedinejad

December 9, 2005
https://p.dw.com/p/BvHH

Jamus da sauran kasashen Turai sun fusata dangane da sabbin kalaman da shugaban Iran Mahmud Ahmedinejad yayi na nuna kyamar Isra´ila. A lokacin da ta ke ganawa da shugaban Faransa Jaques Chirac a birnin Berlin SGJ Angela Merkel ta ce ko kadan kalaman na shugaba Ahmedinejad ba abin karbuwa ba ne. Shi dai shugaban na Iran ya kwatanta Isra´ila da wata cutar cancer sannan ya ce kamata yayi a mayar da kasar ta bani Yahudu cikin nahiyar Turai. Ahmedinejad ya fadawa gidan telebijin din Iran ta El Alam cewa ta haka ne kawai za´a iya warware rikicin yankin GTT. A wasu makonni da suka wuce shugaban na Iran ya sha suka da kakkausar lafazi daga kasashen duniya a dangane da kiran da yayi na a goge Isra´ila daga taswirar duniya.