An yi tir da harin kunar bakin wake na birnin Bagadaza
April 8, 2006Babban sakataren MDD Kofi Annan yayi Allah wadai da harin bam din da aka kai jiya akan wani masallacin ´yan shi´a a birnin Bagadaza wanda ya halaka mutane 79. Annan ya ce manufar maharan shine su haddasa gaba tsakanin al´umomin Iraqi. Harin wanda aka kai akan masallacin Buratha dake birnin Bagadaza shi ne mafi muni cikin watanni 3 kuma wasu ´yan kunar bakin wake su uku su kai harin. Biyu daga cikin su sun yi shiga ce ta mata. Harin ya kuma raunata akalla mutane 150. Jakadan Amirka a Bagadaza yayi gargadin game da barkewar wani yakin basasa tsakanin ´yan shi´a da ´yan sunni, idan kokarin da ake yi na kafa gwamnati ya ci-tura. A dai halin da ake ciki ´yan siyasa na bangaren Sunni da kurdawa sun ki yi aiki da FM rikon kwarya Ibrahim E-Jaafari, wanda yayi watsi da kira da suka yi masa da yayi murabus.