1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi garkuwa da wasu turawa yan yawan shaƙatawa a gabacin ƙasar Niger

August 22, 2006
https://p.dw.com/p/Bulw

Sanarwa daga Opishin ministan harakokin wajen ƙasar italia, ta bayana cewar wasu mutane ɗauke da makamai sun yi awan gaba, da yan yawan shaƙatawa fiye da 20, a gabacin Jamhuriya Niger gap ga iyaka da Tchad.

Al´ammarin ya wakana a yammacin jiya.

Daga cikin turawan da a ka kama, 21 yan ƙasar Italia ne.

Sanarwar ta ce, wani ɗan yawan shaƙatawa [Y1] na ƙasar Jamus, da ya ƙetara rijiya da baya, ya bada wannan labari.

Ya zuwa yanzu, babu labari a hukunce, daga Niger ko kuma Tchad, da ya bada ƙarin haske a game da batun.

Ƙaramin opishin jikadancin Italia dake ƙasar Cote d´Ivoire ya tura tawaga ta mussamman a Jamhuriya Niger, domin samin ƙarin haske.

Sannan Italia, ta shiga tantanawa da opisoshin jikadancin Jamus da na France, da ke birnin Niamey.