An yi batakashi tsakanin magoya bayan Hamas da Fatah
April 22, 2006Talla
´Yan bindiga na kungiyar Hamas dake jan ragamar mulki da aboklan gabarsu na kungiyar Fatah sun yi musayar wuta da jefa nakiyoyi da bama-bamai akan juna a wani artabu da suka yi yau a birnin Gaza. Hakan ta faru ne kwana daya kacal bayan da shugaban bangaren siyasa na Hamas Khaled Mashaal ya zargi shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas da cin amanar al´umar Falasdinu. Akalla mutane 15 sun samu raunuka a arangamar da aka yi. Magoya bayan Fatah sun kwashe ranary au asabar sun a gudanar da zanga-zanga akan tituna don yin tir da kalaman na Mashaal. Da farko sun fara jifar juna da duwatsu sannan daga bisani wasu ´yan bindiga daga bangarorin Hamas da fatah suka fara budewa juna wuta.