1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An tsinci gawar ɗaya daga cikin Jamusawa biyu da aka garkuwa da su a Afghanistan

July 22, 2007
https://p.dw.com/p/BuFm

A ci-gaba da neman ´yan kasar KTK 23 da ake garkuwa da su dakarun Afghanistan da na Amirka sun yiwa wani kauye dake lardin Ghasni kawanya. Wani kakakin ma´aikatar tsaro a birnin Kabul ya ce an san wurin da aka boye mutanen da ake garkuwar da su. A kuma halin da ake ciki an tsinci gawar daya daga cikin Jamusawa biyu da aka yi garkuwa da su a kudancin Afghanistan. Tun dai a jiya ´yan kungiyar Taliban sun ce sun harbe mutanen biyu har lahira bayan da gwamnatoci a Kabul da Berlin suka ki tuntubar ´yan tawayen. Ministan harkokin wajen Afghanistan Rangin Dadfar Spantan yayi tir da garkuwa yana mai cewa.

Spantan:

“Wannan wani aiki ne na dabbanci wanda muke Allah wadai da shi. Al´umar Afghanistan na nuna zumuncin su ga iyalan wadanda abin ya shafa.