An tsare bakin hauren Afirka da dama a Libya
October 8, 2015Talla
Jami'an tsaron kasar Libya sun tsare bakin haure kusan 300 daga kasashen Afirka Kudu da Sahara, wadanda suka boya a wata gona a birnin Tripoli suna jiran wani jirgin ruwa da zai kawo su Turai. Abdel Nasser Hazem shi ne kakakin ma'aikatar yaki da bakin haure a Libya wanda ya yi karin haske.
"Ofishin bincike na birnin Tripoli ya kai samame a wani sansanin bakin haure da ke birnin. Akwai mutane kimanin 289 daga kasashe daban-daban. An kama su kuma an kawo su nan wurin, yanzu haka kuma mun fara shirye-shiryen mayar da su kasashensu na asali."
A kowace shekara dai dubun dubatan 'yan Afirka Kudu da Sahara na bi ta Libya a kokarinsu na neman shigowa nahiyar Turai ta tekun Bahar Rum.