1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An soke ziyarar da Kofi Annan zai kai Iran a makon gobe

November 5, 2005
https://p.dw.com/p/BvMW
Bayan kalaman nuna kyamar Isra´ila da shugaba Mahmud Ahmedi-Nejad na Iran yayi, babban sakataren MDD ya soke ziyarar da ya shirya kaiwa Iran cikin mako mai zuwa. Wata sanarwa da MDD ta bayar a birnin New York ta ce an cimma wannan daidaito ne tsakanin mahukuntan birnin Teheran da mista Annan, cewar bai dace ba babban sakataren na MDD ya kai ziyarar a wannan lokaci. A cikin makon gobe ne dai Annan zai wani rangadin kasashen yankin GTT. A cikin makon jiya kwamitin sulhu na MDD yayi tir da kalaman da shugaba Ahmedi-Nejad yayi na a shafe Isra´ila daga taswirar duniya.