1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An samu daya daga cikin 'yan matan Chibok

Suleiman BabayoMay 18, 2016

An samu daya daga cikin 'yan matan Chibok 'yan makaranta da 'yan Boko Haram suka sace fiye da shekaru biyu a Najeriya.

https://p.dw.com/p/1Iprw
Nigeria Jahrestag Entführte Schulmädchen Boko Haram
Hoto: Reuters/A. Sotunde

Rahotanni daga Najeriya na cewa an samu daya daga cikin 'yan mata 'yan makaranta na Chibok wadanda tsagerun kungiyar Boko Haram suka sace fiye da shekaru biyu da suka gabata.

Kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya ruwaito 'yan gwagwarmya da shugaban al'umma suna tabbatar da labarin. Fiye da shekaru biyu da suka gabata aka sace 'yan mata fiye da 200 a garin Chibok na Jihar Borno da ke yabnkin arewa maso gabashin Najeriya, inda tsagerun na Boko Haram suka yi sanadiyar mutuwar dubban mutane.