1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sace wata mata a yankin Naija Delta

February 8, 2007
https://p.dw.com/p/BuSF

Rundunar yan sanda a Najeriya ta sanarda sace wata mata yar kasar Filipins da wasu yan bindiga sukayi jiya a birnin Fatakwal dake yankin Naija Delta.

Wata mai magana da yawun yan sandan tace yan bindigar sunyi awon gaba da matar ne a lokacinda ta fito daga motarta zata shiga wani banki.

Sace wannan mata ya kawo yawan yan kasashen waje da kungoyoyin suka sace zuwa mutum 30 a yankin na naija Delta.

Wannan kuma shine karo na farko tsageran yankin suka sace mace tun lokacinda suka fara garkuwa da yan kasashen waje a yankin.