An sace wata mata a yankin Naija Delta
February 8, 2007Talla
Rundunar yan sanda a Najeriya ta sanarda sace wata mata yar kasar Filipins da wasu yan bindiga sukayi jiya a birnin Fatakwal dake yankin Naija Delta.
Wata mai magana da yawun yan sandan tace yan bindigar sunyi awon gaba da matar ne a lokacinda ta fito daga motarta zata shiga wani banki.
Sace wannan mata ya kawo yawan yan kasashen waje da kungoyoyin suka sace zuwa mutum 30 a yankin na naija Delta.
Wannan kuma shine karo na farko tsageran yankin suka sace mace tun lokacinda suka fara garkuwa da yan kasashen waje a yankin.