An sace motoci 20 na hukumar bada agaji ta Majalisar Dinkin Dunia a yankin Darfur
February 7, 2006Talla
Hukumar Majalisar Dinkin Dunia mai kulla da bada taimakon abinci, ta nuna damuwa a game da halin da jami´an ta ke ciki a yankin Darhur na kasar Sudan.
Kakakin wannan hukuma, ya bayyana cewa a satin da ya gabata, mutane dauke da makamai sun yi awan gaba, da motoci a kalla 20 mallakar hukumar .
A halin yanzu a cewar sa, hukumar na tallafawa mutane kussan million 3 da abinci,a yankin Darfur, amma a kawai alamun dakatar da talafin, idan a ka cigaba da fuskantar tabarbarewar matakan tsaro.
Shugabanin hukumar, sun tuntunbi magabatan yan tawayen Darfu,r da na gwamnatin Sudan , amma har yanzu babu wani mataki da su ka dauka a kai.