1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An rusa gwamnati a Equitorial Guinea

Zainab A MohammedAugust 11, 2006
https://p.dw.com/p/Bu62

Rahotanni daga Equitorial Guinea na nuni dacewa shugaban kasar Teodoro Obiang Nguema Mbasogo,ya tilastawa prime minista da ministocinsa yin murabus daga mukamansu,wanda zai samar da daman yin garon bawul a gwamnatin wannan kasa dake zama ta 3 a jerin kasashen Afrika masu arzikin man petur.A jiya nedai Shugaba Obiang,wanda ke rike da mulkin Guinea tunda ta samu yancin kai a 1979,a hukuman ya amince da takardun murabus din premier Abia Biteo Borico,da sauran mukarraban gwamnatinsa a wannan kasa dake yammacin Afrika.Shugaba na Guinea dai yasha zargin gwamnatin kasar da rashin inganci musamman a bangaren kula da lafiya da inganta ilimi.Anasaran Shugaba Obiang zai sanar da sabon Prime minista cikin yan kwanaki masu gabatowa.