1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An rantsar da sabon shugaban kasar Angola

Salissou Boukari
September 26, 2017

A wannan Talatan ce sabon shugaban kasar Angola Joao Manuel Gonçalves Lourenço ya yi rantsuwar kama aiki, inda ya canji shugaba José Eduardo dos Santos wanda ya mulki kasar tsawon shekaru 38.

https://p.dw.com/p/2kjvT
Joao Manuel Goncalves Lourenc Verteidigungsminister Angola
Sabon shugaban kasar Angola Joao Manuel Gonçalves LourençoHoto: picture alliance/dpa/R. Jensen

Sabon shugaban dai ya samu wannan matsayi ne bayan da jam'iyyarsa ta MPLA  da ke mulkin kasar tun daga shekara ta 1975  ta yi nasara a zaben majalisar dokokin kasar da ya gudana ranar 23 ga watan Augusta. Bikin rantsar da sabon shugaban wanda shi ne shugaba na uku na kasar ta Angola kuma janar na soja mai ritaya Lourenço, ya wakana ne tare da halartar tsohon shugaban kasar José Eduardo dos Santos, da kuma shugabannin kasashen waje da dama cikinsu har da na kasar Ruwanda Paul Kagame, da na Aquatoriyal Guinea Teodoro Obiang Nguema.