1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An rantsar da sabin hukumomin Thailand

September 22, 2006
https://p.dw.com/p/Buif

Sojojin da su ka gudanar da juyin mulki ranar talata da ta wuce a Thailand, sun samu tabaraki daga sarkin ƙasar.

Bayan ayar dokar da ya sa ma hannu , a yau ɗin nan, aka gudanar da shagulgullan rantsar da sojojin, a matsayin sabin hukumomin da za su jagorancin ƙasar Thailand.

Kamar yadda al´ada ta tanada, saban Praministan, Jannar Sonthi Boonyaratglin, ya sunkuya gaban butun-butumin sarkli domin yi masa mubai´a da da´a.

A nasa ɓangaren hambararen Praminstan,wanda a halin yanzu, ke cikin gudun hijira a kasar Engla, ya rungumi ƙaddara, ya ce kuma a shire ya ke, ya ajje takara, inda aka tashi shirya saban zaɓe.

Saidai Sabin hukumomin ƙasar sun ɗauki mattakai masu tsauri, ga yan siyasa, inda a halin yanzu a ka haramta duk wasu tarruruka na siyasa a fadin ƙasar baki ɗaya.