An nada hukumar bincike a Thailand
September 25, 2006Talla
Shugabannin gwamnatin soji da suka kifar da gwamnatin Thailand,sun kafa hukumar binciken harkokin rashawa da cin hanci a gwamnastin hambararren premier Thaksin Shinawatra.Hukumar nada ikon kwace kaddarorin yan siyasa dana iyalansu.A halinda ake ciki yanzu haka dai uwargidan tsohon premiern Thaland din,ta hade da maigidanta da a yanzu yake London,bayan barin birnin Bangkok.Akwai hasashen cewa Pojaman Shinawatra,tayi taziri wajen tafiyar da ayyukan maigidanta,lokacin da yake mulki.Mafi yawa daga ciki dukiyar da kaddarorin billoniyan dan siyasan na karkashin sunan uwargidansa.