An naɗa saban sarkin musulmi a Nigeria
November 2, 2006Talla
Kwanaki 5 bayan rasuwar mai Daraja Sarkin Musulmi El Haji Muhamadu Macciɗo, hukumomin Nigeria, sun naɗa Kalan Muhamadu Sa´ad Abubakar na 3, a matsayin magajin sa.
Sakataran gwamnatin Jihar Sokoto,Maigari Dingyaɗi, da ya bayyana wannan sanarwa ya ce saban sarkin ya samu mubai´a daga gidajen sarautar baki ɗaya.
Saban sarkin musulmi na 20 Muhamadu Sa´ad Abubabakar na 3 na matsayin ƙane ,ga mirganyi Muhamadu Macciɗo.