An kashe sojoji biyu a Filato
March 15, 2018Talla
Rundunar sojin Najeriyar ta ce ta tura karin wasu dakarunta a karamar hukumar Bassa, bayan samun labarin barkewar sabon tarzoma tsakanin manoma da makiyaya.
Bayan mutuwar sojoji biyu akwai wasu sojoji da suka jikkata a artabun, sabon rikicin ya zo ne kwanaki kalilan bayan wani rikici da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 25 a karamar hukumar Bassa.
Gwamnatin jihar Filato ta sanya dokar takaita zirga-zirga a karamar hukumar Bassa daga shida na safe zuwa shida na yamma, bayan barkewar sabon rikicin.