1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe mutane 20 a Filato

Abdul-raheem Hassan
October 16, 2017

Rahotanni daga birnin Jos da ke tsakiyar Najeriya, na cewa maharan sun kai hare-haren ne a ranakun Lahadi da kuma yau Litinin, inda suka kashe mutane sama da 20, tare da jikkata wasu a kauyukan karamar hukumar Bassa.

https://p.dw.com/p/2lwA1
Nigeria Soldaten
Hoto: picture-alliance/dpa

'Yan bindigan sun farawa mutanen kauyukan wadan ke neman mafaka a wata makarantar firamare cikin masarautar Irigwe. Kawo yanzu dai babu cikkakun bayanan jamai'an tsaro kan adadin mutane da suka mutu a harin, amma dai gwamnatin jihar Filato ta kafa dokar hana zirga zirgar a karamar hukumar ta Bassa daga karfe shida na yammaci zuwa shida na safiya.