1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: An kashe mayakan Boko Haram

Abdourahamane HassaneJuly 10, 2016

Rundunar sojojin Najeriya ta ce mayakanta sun kashe 'yan kungiyar Boko Haram guda16, kana su kuma a bangaransu sun samu asarar rayuka na sojoji guda biyu.

https://p.dw.com/p/1JMS3
Nigeria Boko Haram Terrorist
Hoto: picture alliance/AP Photo

Hakan kuwa ya biyo bayan farmakin da mayakan kungiyar ta Boko Haram suka kai a garin Rann da ke cikin karamar hukumar Kalabalge cikin jihar Borno da ke yankin arewa maso gabshin Najeriya, wanda ke kan iyaka da Kamaru. Masu aiko da rahotannin sun ce mayakan na Boko Haram sun shiga garin ne na Rann a kan babura inda suka bude wuta a kan mai uwa da wabi.Kafin daga bisanni su yi yunkurin kai hari a kan wani sanssanin soji sai dai sojojin Najeriya suka taka musu birki. Yanzu haka jama'a da dama mazauna garin na Rann, sun tsere zuwa Kamaru domin samun mafaka bayan afkuwar wannan hari.