1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kammala taron kolin kungiyar D-8 a tsibirin Bali

May 13, 2006
https://p.dw.com/p/BuyV
Taron kolin kungiyar D-8 ta kasashe masu tasowa wadanda musulmi suka fi rinjaye a cikin su, bai tattauna kai tsaye game da takaddamar da ake yi akan shirin nukiliyar Iran ba. Shugaban Indonesia Susilo Bambang Yudhoyono ya bayyana haka a wani taron manema labarai a karshen taron kungiyar ta D-8 da ya gudana a tsibirin Bali na kasar ta Indonesia. Mahalarta taron kolin sun tattauna akan batutuwan da suka hada da hauhawar farashin mai a duniya da dangantaka tsakanin musulmi da sauran kasashen duniya. Shugaban Indonesia wanda ya karbi ragamar shugabancin kungiyar daga shugaba Mahmud Ahmedi Nijad na Iran, yayi kira da a samar da kyakkyawan yanayin tuntubar juna tsakanin mabiya addinai da kuma al´adu dabam-dabam. Kungiyar ta D-8 ta kunshi kasashen Bangladesh, Masar, Indonesia, Iran, Malaysia, Nigeria, Pakistan da kuma Turkiya.