An kame jagoran masu zanga-zanga a Maroko
May 29, 2017A kasar Maroko an cafke jagoran zanga-zangar nan da aka kwashe watanni da dama ana yi. Majiyoyin gwamnati sun ce 'yan sanda sun kame Nasser Zefzafi mai shekaru 39 da haihuwa. A ranar Jumma'a da ta gabata mahukunta suka bada sammacin kame dan gwagwarmayar bayan da ya kawo tsaiko lokacin hudubar wani limani a wani masallacin Jumma'a da ke birnin Al-Hoceima, inda kwanaki uku a jere a ranar Lahadi daruruwan mutane suka fantsama kan titunan birnin suna sowa suna zargin yawaitar cin hanci da rashawa a kasar. Zanga-zangar da ta kasance karkashin jagorancin Zefzafi a watannin bayan nan, na da nasaba da rashin aikin yi, da tabarbarewar sha'anin kiwon lafiya da matsalar cin hanci da rashawa a yankin arewacin kasar ta Maroko. Da yammacin ranar Lahadi an yi zanga-zanga a wasu biranen ciki har da Rabat babban birnin kasar.