An kamamla taron kasashen Afirka da na Turai a rabat
July 11, 2006Talla
Kasashe 57 na Turai da Afirka sun amince da wani gagarumin shirin rage kwararar ´yan gudun hijira zuwa nahiyar Turai. Shirin wanda aka amince da shi a gun babban taron da sassan biyu suka yi a birnin Rabat na kasar Marokko ya tanadi ba da karin taimakon raya kasa ga kasashen masu tasowa na Afirka tare da Skarfafa hadin kai a yaki ga kungiyoyi masu fataucin ´yan Adam. Hakazalika an amince da kara daukar tsararan matakan tsaron kan iyakoki. To sai dai shirin bai yi bayani game da kudin da za´a ware ga wannan aiki ba.