1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kama wani dan Najeriya a Jamus

Gazali Abdou Tasawa
February 9, 2017

'Yan sanda a nan Jamus sun kame wasu mutane biyu daya dan kasar Aljeriya daya kuma dan Najeriya a bisa zarginsu da shirya kai wani harin ta'addanci a cikin kasar. 

https://p.dw.com/p/2XF1p
Zwei Salafisten in Göttingen festgenommen
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Rampfel

An kama mutanen ne a wannan Alhamis a lokacin wani sumame da 'yan sanda 450 suka kai a birnin Göttingen na tsakiyar kasar bayan da suka samu wasu bayanan sirri da ke nuna cewar mutanen wadanda mambobin Kungiyar Musulmi Salafawa ne na shirin kitsa kai wani hari a kasar. 

Mutane kimanin 550 ne masu alaka da Kungiyar Salafawa a Jamus mahukuntan kasar suka jera a jerin sunayen mutanen da ke a matsayin wata babbar barazana a kasar. 

Kasar Jamus wacce sannu a hankali Musulmi masu akidar Salafanci ke yaduwa a cikinta a 'yan shekarun baya bayan nan, ta fuskanci jerin hare-haren ta'addanci wadanda Kungiyar IS ta dauki alhakin kai su.