1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hari kan kotun gudanarwa a Turkiya

May 17, 2006
https://p.dw.com/p/Buxu

An kashe wani alkali sannan aka yiwa abokanen aikin sa su 4 rauni a wani hari da aka kai kan babbar kotun gudanarwa dake birnin Ankara a can kasar Turkiya. ´Yan sanda sun cafke wanda ya kai harin. Kafofin yada labaru sun labarto cewa mutumin da ya kai harin wani mai tsattsauran ra´ayin addinin Islama ne wanda ya taba aiki a mastayin lauya a cikin kasar. Sau da yawa dai masu kishin Islama kan kaiwa kotun gudanarwar hare hare musamman saboda hukunci da ta ke yankewa na goyon bayan tsarin rayuwa ta ´yan kasashen yamma kamar haramta daura dan kwali. Shugaban kasa Ahmet Necdet Sezer ya ce tsarin shari´ar kasar ta Turkiya ba zai saduda ga bukatun masu kishin addini ba.