1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kaddamar da saban kundin tsarin mulki a Jamhuriya Demokradiyar Congo

February 18, 2006
https://p.dw.com/p/Bv7f

Shugaban Jamhuriya demokaradiyar Congo, Joseph kabila, ya kaddamar da saban kundin tsarin mulkin kasa, wadda ke matsayin mataki mai tasiri ta fannin girka inganttatar demokradiya a wannan kasa.

A watan desember ne da ya wuce, al´ummar ,ta kada kuri´ar amincewa da wannan saban kundin tsari mulki, da kashi 84 bisa 100, na wanda su ka yi zaben.

Kudin ya tanadi shinfida mulki mai ruwa 2 , bisa jagorancin shugaban kasa da Praminista.

Wannan mataki da aka cimma, zai bada damar shirya zabbuka daban daban a kasar, kamin karshen watan juni mai zuwa, wanda a sakamakon su, a ke kyauttata zaton Jamhuriya demokradiyar Congo ta bi sahun kasashen masu tafarkin demokradiya bayan yake yaken bassasa , da kuma mulki rikwan kwarya, na tsawan shekaru 3.