An halaka masu zanga-zanga su kimanin 17 a kasar Guinea
January 22, 2007A wani mataki na murkushe wani boren nuna kyamar shugaban jamhuriyar Guinea Lansane Conte ´yan sanda a kasar da ke yammacin Afirka sun kashe masu zanga-zanga su 17. wata sanarwa da likitoci da kuma kungiyoyin ma´aikata suka bayar ta ce ´yan sanda sun harbe masu zanga zangar ne har lahira a wajen Conakry babban birnin kasar. Tun fara wani yajin aikin gama gari da kungiyoyin ma´aikata suka kira kusan makonni biyu da suka wuce, an halaka mutane kimanin 30 a kasar ta Guinea. Jam´iyun adawa 14 na goyon bayan yajin aiki na sai baba ta gani, wanda aka shirya da nufin tilastawa shugaba Conte wanda ya haye kan karagar mulki tun a shekarar 1984, da yayi murabus. Ana zargin shugaban mai shekaru 72 da laifin cin hanci da rashawa da kuma rashin iya mulki.