1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takunkumi kan masu cinikin bayi a Libiya

Abdul-raheem Hassan
June 8, 2018

Matakin Majalisar Dinkin Duniyan ya bukaci toshe asusun bankin mutane da ke jagorantar kungiyoyin safarar bakin haure, tare da haramta musu tafiye-tafiye a kasashen ketere.

https://p.dw.com/p/2z861
Libyen Flüchtlinge
Hoto: picture-alliance/dpa

Wannan dai shi ne karo na farko da kwamitin sulhu na MDD ya fara daukar matakin ayyana takunkumi kan daidaikun kungiyoyi tare da takunkumi kan laifukan safarar jama'a.

Kasar Libiya ta yi kaurin suna wajen cinikin bakin haure bayan da kafar talabijin na CNN, ta wallafa bidiyon yadda ake gwanjon 'yan ci ranin Afirka a shekarar 2016.