1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

2026: Kasashe 3 za su karbi bakuncin gasar kwallo

Ramatu Garba Baba
June 13, 2018

Amirka da Mexico da kuma Kanada sun buge kasar Moroko inda kasashen da suka shigar da bukatar hadin gwiwar za su dauki bakuncin gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya a shekarar 2026.

https://p.dw.com/p/2zU5E
Russland, Moskau: Wahl zum FIFA World Cup 2026
Hoto: picture-alliance/AP Photo/A. Zemlianichenko

Hukumar FIFA ce ta sanar da hakan a wannan Laraba bayan da aka kada kuri'a kuma gamayar kasashen ukun suka sami yawan kuri'u dari da talatin da hudu da suka zarta Moroko mai kuri'u sittin da biyar, an kada kuri'a a birnin Moscow na kasar Rasha gabanin soma gasar 2018 da Rashan ke daukar nauyinta.

Wannan shi ne karo na biyar da kasar ta Moroko ke shan kaye bayan ta kai wannan mataki amman kuma ta gagara samun damar daukar nauyin gasar.