1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An damke masu shirin ta'addanci a Jamus

Yusuf BalaSeptember 13, 2016

Sama da 'yan gudun hijira miliyan guda sun shiga Jamus inda a cikinsu ake zargi akwai bara gurbi, da ke fakewa da neman mafakar siyasa dan aika-aika.

https://p.dw.com/p/1K1D9
Thomas de Maiziere PK Razzia NRW in Berlin
Ministan harkokin cikin gidan JamusThomas de MaiziereHoto: picture-alliance/dpa/M.Kappeler

Wasu masu neman mafakar siyasa uku a Jamus sun zo hannun mahukunta a bisa zargin shirye-shirye na kitsa kai harin ta'addanci a madadin Kungiyar IS, an kuma gano cewa suna da alaka da harin da aka kai a birnin Paris na kasar Faransa a cewar ministan harkokin cikin gidan Jamus Thomas de Maiziere.

Da yake jawabi a ranar Talatan nan de Maiziere ya ce tsawon watanni uku da aka dauka ana bincike an gano cewa mutanen masu shekaru 17 da 18 da 26 sun sami dama ta shigowa Turai ne ta hanyar masu fasakauri da suka shigo da wadanda suka kai hari a Paris a watan Nuwamba, harin da ya yi sanadi na kisan mutane 130. Kuma takardun bogi da suka yi amfani da su dan shigowa Turai an yi su a wuri guda.