1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An dakatar da aikin agaji a wasu yankuna biyu na Kashmir

January 7, 2006
https://p.dw.com/p/BvDO

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta dakatar da aikin ba da taimako a wasu yankuna biyu dake bangaren Pakitsan a lardin Kashmir wanda ke fama da masifar girgizar kasa. MDD ta dauki wannan mataki ne bayan da wasu kauyawa suka farma jiragen samanta masu saukar ungulu a wannan yanki. Su dai kauyawan sun nemi a kwashe su ne daga yankin. Wani kakakin MDD ya ce za´a katse dukkan jigilar kai agaji ta sama zuwa yankin Lipa don tabbatar da tsaro da lafiyar ma´aikata da kuma matukan jiragen saman masu saukar ungulu. Mutane fiye da dubu 73 suka mutu yayin da miliyoyi suka yi asarar gidajensu sakamakon mummunar girgizar kasar da ta auku a yankin a cikin watan okotoban bara. Yanzu haka dai miliyoyin mutane na zaune ne a cikin wani yanayi na matsanancin sanyin hunuturu karkashin tantuna da aka kakkafa.