1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

280910 Guinea Massaker Jahrestag

September 28, 2010

Kwana tashi yau shekara guda kenan da sojojin Guinea su ka aikata kisan gilla kan mutane da dama a yayin wani taron gangami.

https://p.dw.com/p/POp6
Sojojin Guinea sun hallaka mutane 165 a sheakar baraHoto: AP

Ƙungiyar Kare haƙƙin bil Adama ta Human Wrights Wacht ta bukaci hukumomi a ƙasar Guinea da su tabbatar da hukunci ta  hanyar yiwa  waɗanda  a ka samu da laifin aikata kisan gilla a lokacin zanga zanga da aka gudanar a ƙasar a bara.

Sanarwa da Ƙungiyar ta bayyana, wacce ta zo a daidai lokacin da ake gudanar da zaman  juyayin a yau na zagayawar cikon shekara guda da aikata kisan gillar da sojojin  Musa Dadis Camara su ka aikata a ranar 28 ga watan Satumba  na shekara ta 2009,  akan jama´ar ƙasar ta Guinea na zaman ƙara jan hankali hukomomin.

Mutane a ƙalla 156, galibi ´yan adawa su ka rasa rayukansu a cikin zanga zangar.

Ibrahim Bary na ɗaya daga cikin waɗanda su ka tsira da rayukansu.

Ni ina ganin duk wanda ya aikata kisan gilla to ya kamata a hukunta shi, ya ce a lokacin zanga- zangar mun ga manyan sojoji da ministan tsaro su na bada umarni, amma kuma ya ce har yanzu ba a hukunta su ba.

Mawallafi: Abdourahman Hassane

Edita: Yahouza Sadissou Madobi