1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bukaci a zauna lafiya a Kenya

Ramatu Garba Baba
September 22, 2017

Shugaba Uhuru Kenyatta na Kenya zai ci gaba da jan ragamar mulkin kasar sai in har an sami sauyi a babban zaben da ake shirin gudanarwa nan gaba.

https://p.dw.com/p/2kXgH
Kenias Oberstes Gericht
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Azim

Babban Antoni Janaral na kasar ta Kenya Guthi Muigaia ya sanar da wannan mataki  a wannan Juma'ar a yayin taron manema labarai, wannan na zuwa ne a daidai lokacin da al'umma ke zaman dar-dar gudun abinda ka iya biyo baya bayan sanarwar dage zaben da hukumar zaben kasar ta fitar a jiya Alhamis, hukumar ta ce an dage zaben ne biyo bayan bayanai mai dauke da sarkakiya da kotun kolin kasar ta bayyana a ranar Larabar da ta gabata hakan na nufi za a gudanar da zaben shugaban kasar a ranar 26 ga watan Oktoba.