1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bude sake famfo a birnin Harbin na kasar China

November 27, 2005
https://p.dw.com/p/BvJD

Rahotanni daga China sun ce an sake bude ruwan fanfo a birnin Harbin wanda yayi fama da hadarin gubar Benzin. Kamar yadda kamfanin dillancin labarun kasar Xinhua ya rawaito, an bude famfo sa´o´i biyar gabanin lokacin da aka tsara da farko. To sai dai duk da haka hukumomi sun yi kira da a yi takatsantsan wajen shan ruwan famfo. Rahotanni sun ce yanzu haka dai ruwan kogin Songhua da ya gurbace da sinadarin Benzin, ya wuce birnin na Harbin. A tsakiyar makon jiya aka dauke ruwan famfo a birnin gabaki daya don kare mazauna daga gubar ta Benzin.