1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An buda runfunan zaben rabagardama a Burtaniya

Salissou BoukariJune 23, 2016

A wannan Alhamis din ce 'yan kasar Burtaniya kusan miliyan 46 da dubu 500, za su kada kuri'unsu a zaben raba gardama kan ci gaba da kasancewar kasar a Tarayyar Turai.

https://p.dw.com/p/1JBci
Großbritannien EU-Referendum Brexit - Wahlkampf Vote Leave-Kampagne in London
Hoto: DW/C. Ricking

Tun shekaru da dama ne masu adawa da kasancewar kasar ta Burtaniya cikin Tarayyar Turai ke ta nema da a yi wannan zaben raba gardama, wanda kuma a baya Firaministan kasar David Cameron ya sha alwashin gudanar da shi.

Wannan zabe dai zai taka babbar rawa kan makomar siyasar kasar ta Burtaniya, da ma ta Tarayyar Turai, wanda ake ganin idan har masu ra'ayin ficewa suka yi rinjaye, to kasar ta Burtaniya da Tarayyar Turai za su shafe tsawon shekaru wajen tattauna matakan wannan rabuwa mai cike da sarkakiya.