Amon harbe-harbe a birnin Bouake
May 15, 2017Talla
Sojoji a Ivory Coast sun durfafi birni na biyu mafi girma a kasar a wani mataki da babban hafsan sojin kasar ya ce sun kaddama na kawo karshen boren da wasu sojojin suka yi na tsawon kwanaki uku game da biyan su wasu kudaden su na garabasa.
Akalla mutane biyar aka bada rahoton sun rasu sakamakon harbin bindiga a birnin Bouake lokacin da sojojin suka kaddamar da bore. Al'umma a kasar na cigaba da gangamin nuna adawa da boren sojin.
Jama'a a biranen Abidjan da kuma Bouake sun ce sun ji amon harbe-harben bindiga da safiyar yau Litinin abin da ke nuna cewa har yanzu kurar ba ta lafa ba.