Amirka zata tura wakiliyarta ta musamman zuwa Khartoum
August 25, 2006Shugaban Amirka GWB zai tura wata wakiliyar sa ta musamman zuwa Sudan don matsa lamba ga shirin girke dakarun MDD a lardin Darfur mai fama da rikici. A halin da ake ciki wakiliyar ma´aikatar harkokin wajen Amirka akan nahiyar Afirka Jendayi Frazer ta sanar cewa a yau juma´a zata tashi zuwa birnin Khartoum. A cikin sanawar da ta bayar Frazer ta ce dole ne a dauki sahihan matakan kare al´umar yankin na Darfur daga kisan kare dangi da ake yi a can. Tuni dai Amirka da Birtaniya suka gabatarwa kwamitin sulhun MDD wani daftarin kuduri game da tura sojoji dubu 17, don maye gurbin dakarun kungiyar tarayyar Afirka da aka girke a Darfur dake yammacin Sudan. Har yanzu kuwa gwamnatin Sudan na adawa da girke dakarun na MDD. A ranar litini mai zuwa kwamitin sulhu zai zama na musamman kan wannan batu.