1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta rage sojojinta a Koriya ta Kudu

Abdul-raheem Hassan
May 4, 2018

Jaridar New York Times ta ruwaito Shugaban Amirka Donald Trump ya umarci ma'aikatar tsaro ta Pentagon ta fara shirin janye wasu dakarun kasar da ke a yankin Koriya

https://p.dw.com/p/2x9UO
US-Stützpunkt Humphreys in Südkorea
Hoto: picture-alliance/dpa/epa/US 2nd Infantry Division

Sai dai sun bayyana cewa batun rage yawan dakarun Amirka baya cikin jadawalin ganawar shugaba Trump da shugaban Koriya ta Arewa a tsakanin karshen watan Mayu ko Yuni. Sai dai ana ganin tattaunawar neman dinke baraka tsakanin Amirka da koriyoyin biyu, zai yi tasirin janye sojojin Amirka dubu 23 da ke jibge a yankin.

Sai dai ana nuna shakku kan cire sojojin Amirka baki daya daga yankin ba tare da samun tabbacin warware matsalar tsaro a tsakanin kasashen biyu ba. Fadar White House da kuma ma'aikatar tsaron Amirka ba su yi martani kan batun shirin rage yawan sojojin Amirka da ke aiki a yankin Koriya ba.