1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta kara sojojinta a Nijar

Abdul-raheem Hassan
October 24, 2017

Ma'aikatar tsaro ta Pentagon za ta karfafa matakan tsaro ta hanyar kara jibge wasu dakarunta a kan iyakar kasashen Nijar da Mali, da zummar tallafa wa jamai'an tsaron kasar yakar masu haifar da barazanar tsaro.

https://p.dw.com/p/2mNj4
Soldaten im Niger
Hoto: Desmazes/AFP/Getty Images

Wannan mataki na Amirka na zuwa ne kwanani kalilan bayan wasu jerin hare-haren kwantan bauna da wasu 'yan bindiga suka kai kan iyakar Nijar da Mali, inda suka kashe dakarun Amirka hudu tare da wasu sojojin Nijar a farkon watan Oktoba.

A yanzu dai Pentagon na shirin girke karin wasu dakaru 800 a Nijar da wasu sauran kasashen Afirka, da nufin murkushe ayyukan ta'addancin kungiyar IS da ke zama karfen kafa a wasu kasashe da ke gabashi da yammacin nahiyar ta Afirka baki daya.