1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta horas da sojin Najeriya

Ahmed SalisuAugust 4, 2015

Shugaban tawagar 'yan majalisar dokokin Amirka da ke ziyara a Najeriya ya ce a shirye Amirka ta ke ta tallafawa dakarun Najeriya da horo don kawar da ta'addanci.

https://p.dw.com/p/1G9WZ
Nigeria Soldaten in Diffa
Hoto: Reuters/J. Penney

Dan majalisa Darrell Issa da ke jagorantar tawagar ya ce dakarun na Najeriya sun fi bukatar horo maimakon makamai wajen samun nasara a yakin da suke da 'yan ta'adda wanda suka yi sanadiyyar rasuwar dubban mutane a kasar da kuma kasashen da ke makotaka da ita.

Wadannan kalamai na Mr. Issa na zuwa ne bayan shi da 'yan tawagarsa sun yi wata ganawa da shugaba Muhammadu Buhari da manyan jami'an tsaron kasar kan halin da tsaro a Najeriya ke ciki.