1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta nemi 'ya'yanta da su kaurace wa Kabul

Kamaluddeen SaniApril 11, 2016

Ofishin jakadancin Amirka a kasar Afganistan yayi gargadin cewar mai yiwuwa ne mayakan sa kai su kai wani hari a kan Amerikawa da ke wani otel a Kabul.

https://p.dw.com/p/1ITRV
Ryan Crocker
Hoto: AP

Ofishin jakadancin ya kara da cewar ya na shawarartar duk wasu Amerikawa da su kaucewar otel din tare da zama cikin shirin ko ta kwana a yayin da suke halartar gidajen otel a birnin na Kabul.

Shi dai wannan gargadin na zuwa ne bayan wasu rokoki da aka harba a yankin da ofisoshin Diplomasiya suke a ranar asabar din nan jim kadan bayan Sakataren harkokin wajen Amirka John Kerry ya gudanar da wani taro da Shugabanin kasar ta Afghanistan a birnin Kabul.