1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka da Turkiyya sun sasanta kan Visa

Abdul-raheem Hassan
November 6, 2017

A wata sanarwa da ofishin jakadancin Amirka da ke birnin Ankara ta wallafa a shafin ta na yanar gizo, ta ce ta sassauta matakan haramta wa juna ba da takardar shiga kasashen biyu bayan samun tabbacin ingancin tsaro.

https://p.dw.com/p/2n8or
USA trump und Erdogan Treffen in New York
Hoto: Reuters/K. Lemarque

Wannan matakin sassauta matakai na musanyar samun damar shiga kasashen biyu na zuwa ne kwana guda bayan ganawar Firaiministan Turkiyya Binali Yildirim a birnin Washington, tare da mataimakin shugaban kasar Amirka Mike Pence. A baya dai Yildirim ya nuna takaici kan irin tsamin dangantaka da ke tsakanin kasashen biyu ke shafar harkokin diflomasiya.

Kasashen Turkiyya da Amirka da ke zama mambobin kungiyar tsaro ta Nato, sun kasashece cikin takun saka bayan da hukumomin Turkiyya suka rika kame 'yan Amerika da ke shiga kasar bisa zargin alaka da kungiyar malamin addininnan dan aksar Turkiyya da ke samun mafaka a Amirka, malamin da gwamnatin shugaba Raccep Tayyib Erdogan suka daura alhakin yunkuri juyin mulki a shekarar 2016.