1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ambaliyar ruwa a Dresden a Kasar Jamus

April 1, 2006
https://p.dw.com/p/Bv3U

Rahotanni daga Jihar Saxony dake gabashin Jamus sun shaidar da cewa har yanzu mutanen yankin na cikin hali na kaka ni kayi a sakamakon mummunan ambaliyar ruwa daga kogin Elbe.

Rahotanni sun nunar da cewa ambaliyar ruwan ya zuwa yanzu ta kai tsawon mita a kalla bakwai.

Ya zuwa yanzu dai bayanai sun nunar da cewa babu tabbas ko a nan gaba tunkoron ambaliyar ruwan ka iya kaiwa tsawon mita takwas ko kuma a´a.

A waje daya kuma, bayanai daga makociyar kasar ta Jamus wato kasar Czech, na nuni da cewa mutane hudu ne suka rasa rayukan su a sakamakon ambaliyar ruwan daya shafi wai yanki na kasar.