1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ambaliyar Ruwa a Afrika

September 26, 2007
https://p.dw.com/p/BuAB

Kungiyar bada agajin kasa da kasa ta red cross,tayi gargadi dangane da bukatar samarda agajin gaggawa na abinci wa kasashe yammaci da gabashin Afrika da suka fuskanci matsalar ambaliyar ruwa,kuma ke cigaba da kasancewa ciki.Headquatar kungiyxar Red Cross dake dake birnin Geneva ta bayyana halin kunci da Ghana da Sudan da Uganda ,wadanda ke cikin kasashe 22 da ke fuskantar ambaliyan ke ciki,inda akalla mutane million 1.5 ke bukatar tallafi.Kungiyar dai tace wannan ambaliyan ruwa ya lalata gonakin abinci,adangane da hakane ya dace kungiyoyi da hukumomin bada agaji su kasance cikin shirin kota kwana ,adangane da halin karancin abinci da zaa fuskanta a wadannan kasashen.