1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Alamar samun masalaha a yankin Koriya

Zulaiha Abubakar
January 2, 2018

Shugaba Moon Jae-In na kasar Koriya ta Kudu ya amsa goron sulhuta rikicin yankin in da ya bayyana ce matakin sulhu da makobciyar ta nema abu ne da zai inganta alaka tsakanin kasashen biyu da kuma alamar kauce wa yaki

https://p.dw.com/p/2qFW1
Nordkorea Kim Jong Un
Hoto: Reuters/KCNA


Tun a jawabin sabuwar shekara shugaban kasar Koriya ta Arewa, ya nuna yunkurin yin amfani da kakar wasannin Olympics mai zuwa da za a gudanar a kasar Koriya ta Kudu don daidaita dangantaka tsakanin kasashen.

Bayan shekara guda da ya kwashe yana barazanar makaman kare dangi, a halin yanzu shugaba Kim Jong Un na kasar Koriya ta Arewa ya yi amfani da sakon sa na 2018 dayin kira da a samu kyakykyawar alaka a yankin Koriya, ya kuma kara da jaddada kudirin kasar na bada gudunmawa wajen gudanar da wasannin masu zuwa.

A nata bangaren kasar Koriya ta Kudu dama ta dade tana neman wannan dama daga makobciyar ta ta Koriya ta Arewa, don ganin ba a kassara kasar wasannin ba da wani gwajin na makami mai linzami, don haka shugaban kasarsu ya yi saurin yin maraba da tayin sulhu da Koriya ta Arewa.