Al-uman ƙasar Georgia sun gudanar da zanga zanga.
January 13, 2008Talla
ɗaruruwan dubban magoya bayan jam’iyun adawa sun gudanar da zanga-zanga a babban birnin Georgia, don nuna ƙin amincewarsu game da sakamakon zaben shugaban ƙasa da aka gudanar ranar 5 ga watan janairu. Jam’iyun adawa, sun ce maguɗi da rashin adalci ya sa aka baiwa shugaba Saakashvili mai samun goyan baya daga Amirka nasarar lashe zaben don yin tazarce.
Masu zanga-zangan sun yi maci a kann titunan Tiblis, inda suka yi kira da a sake ƙidayar kuri’un. Sakamakon zaben da aka bayyana ɗazunnan, ya baiwa shugaba Saakashvilli kashi 53 cikin ɗari na ƙuri’un da aka kaɗa, a yayin da shugaban adawa Levan Gachechiladze ya tashi da kashi 25 cikin dari.