1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al-Shabaab ta musanta kashe 'ya'yanta

November 12, 2017

Kungiyar al-Shabaab a kasar Somaliya, ta musanta ikirarin da wata rundunar da Amirka ke jagoranta ta yi na kisar 'ya 'yan kungiyar a wani farmaki da ta kaddamar ta sama a kasar.

https://p.dw.com/p/2nU7p
Al-Shabaab Kämpfer in Mogadishu
Hoto: picture-alliance/AP Photo/AP Photo/F. Abdi Warsameh

Sheikh Abdiasisi Abu Mus'ab da ke zaman wani kusa a kungiyar ta al-Shabaab ne ya musanta ikirarin, inda kuma ya zargi gwamantin Somaliya da zuki-ta-malle kan harin da aka ce an kaddamar kan kungiyar a babbar tungarsu da ke Jilib a Kudu da Mogadishu babban birnin kasar. A wannan Asbara din ne gwamnatin kasar Somaliyar ta sanar da nasarar halaka mayakan na al-shabaab 81. Ita ma Amirka a ranar Alhamis ta sanar da kai wani farmaki kan kungiyar. Cacar baka kan nasarorin kaddamar da hare-hare tsakanin gwamnatin Somaliya da bangaren na al-Shabaab dai ba sabon abu bane, inda galibi ake gaza iya tantance hakikanin gaskiyar lamarin.