1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Aikin Hajji: 'Yan Iran sun isa Saudiyya

Ahmed Salisu
August 29, 2017

Dubban 'yan Iran sun shiga kasa mai tsarki da nufin sauke farali a aikin hajjin bana daidai lokacin da Riyadh da Tehran ke kokari wajen jingine rikicin diflomasiyyarsu.

https://p.dw.com/p/2j0cc
Saudi Arabien Mekka Pilger Kaaba
Hoto: picture alliance/AP Photo/N. El-Mofty

Hukumomi Saudiyya suka ce kimanin alhazan Iran dubu 86 ne suka isa kasar don yin aikin hajjin tare da miliyoyin mahajatta da suka fito daga sassan duniya daban-daban. Al'ummar Iran da dama dai sun bayyana jin dadinsu game da wannan cigaban da aka samu inda da dama ke cewar dama bai kamata rikicin diflomasiyya ya shafi harkoki na addini ba. A shekarar da ta gabata dai 'yan Iran din ba su samu sukunin zuwa yin aikin hajji ba sakamakon rashin jituwa tsakanin mahukuntan Tehran da na Riyadh da kuma gaza amincewa da bangarorin biyu suka yi kan wasu tsare-tsare na aikin hajji.