1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ahmed Shafiq na Masar zai tsaya takara

April 26, 2012

Tsohon firaministan Masar da ya yi aiki ƙarƙashin Hosni Mubarak ya samu izinin tsayawa takara. lamarin da ya saɓa wa dokar da majalisa ta kafa.

https://p.dw.com/p/14l8A
campaign election posters for presidential candidates Ahmed Shafiq in Cairo April 5, 2012. The presidential election will be held on May 23 and 24. REUTERS/Amr Abdallah Dalsh (EGYPT - Tags: POLITICS ELECTIONS) // Eingestellt von wa *** ACHTUNG: Vor allem das Alternativbild hat eine schlechte Bildqualität, besser nicht verwenden ****
Ahmed Schafik ya daɗe da yin postaHoto: Reuters

Hukumar zaɓen Masar ta amince da takarar firaministan da ya yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin hambararren shugaba Hosni Mubarak a zaɓen shugaban ƙasar da za'a gudanar a watan Mayu idan Allah ya kai mu, abun da ya juya shawarar da ta fara yankewa akan dan takarar. Ahmed Shafiq yana daga cikin jami'an gwamnatin da ke aiki lokacin da guguwar neman sauyi ta kaɗa a ƙasar daga farkon shekarar 2011, ta kuma kai ga hamɓarar da Mubarak daga karagar mulkin Masar.

Wannan shawarar dai ta saɓa wa dokar da majalisar dokokin ƙasar ta kafa, wacce ta haramta wa duk wani wanda ya riƙa babban muƙami ƙarƙashin gwamnatin Mubarak takara a zaɓen bana. Kawo yanzu dai 'yan takara 10 ne hukumar zaɓen ta dakatar bisa dalilai daban-daban. Amma kuma ana sa ran a wannan alhamis zata kammala tantance 'yan takarar, ta kuma gabatar da wadanda ta amince da su.

Mawallafi: Pinado Abdu-Waba
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe