1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Zuma zai kalubalanci hukuncin babbar kotu

Yusuf BalaMay 24, 2016

A wani jawabin da ofishin shugaban ya fitar a yammacin ranar Litinin ya ce matakin da kotun ta dauka wani abu ne da ya shafi mutuncin shugaban kai tsaye.

https://p.dw.com/p/1ItMv
Jacob Zuma Korruption Prozess
Shugaba Jacob Zuma na Afirka ta KuduHoto: Getty Images/AFP/R. Jantilal

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma ya bayyana shirin kalubalantar kotun kasar da ta nemi a sake nazarin shari'ar da ake zarginsa da laifukan da suka shafi cin hanci da rashawa da suka tasamma 800 kamar yadda ofishin shugaban ya bayyana.

A wani jawabin da ofishin shugaban ya fitar a yammacin ranar Litinin ya ce matakin da kotun ta dauka wani abu ne da ya shafi mutuncin shugaban kai tsaye, kuma kotun na yin kuskure a wasu ayyukanta.

A watan da ya gabata ne dai babar kotun kasar ta Afirka ta Kudu ta bayyana bukatar sake nazarin tuhume-tuhume da ake wa shugaban wadanda aka ajiye su a shekarar 2009, matakin da babbar kotun ta ce an yi shi ne bisa kuskure.

Masu gabatar da kara a kasar dai ta Afirka ta Kudu sun bayyana cewa za su kalubalanci hukuncin kotun da ke tuhumar shugaba Jacob Zuma da wadannan laifuka, matakin da ya samu suka a kasar, abin da ake ganin kokari ne na ba wa shugaban wata dama ta hana doka ta yi aiki a kansa.